< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Furahini katika Yahwe, ninyi wenye haki; kusifu kwa wenye haki kwa faa sana.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Mshukuruni Bwana kwa kinubi; mwimbieni sifa kwa kinubi chenye nyuzi kumi.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Mwimbieni yeye wimbo mpaya; pigeni kwa ustadi na muimbe kwa furaha.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Kwa kuwa maneno ya Mungu ni ya hakika, na kila afanyacho ni haki.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Yeye hupenda haki na kutenda kwa haki. Dunia imejaa uaminifu wa agano la Yahwe.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Kwa neno la Yahwe mbingu ziliumbwa, na nyota zote ziliumbwa kwa pumzi ya mdomo wake.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Yeye huyakusanya maji ya baharini kama rundo; naye huiweka bahari katika ghala.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Basi ulimwengu wote umwogope Yahwe; wenyeji wote wa ulimwengu wamuhofu yeye.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Kwa maana yeye alisema, na ikafanyika; aliamuru, na ikasimama mahali pake.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Yahwe huvunja muungano wa mataifa; naye huishinda mipango ya wanadamu.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Mipango ya Yahwe husimama milele, mipango ya moyo wake ni kwa ajili ya vizazi vyote.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Limebarikiwa taifa ambalo Mungu wao ni Yahwe, watu ambao yeye amewachagua kama warithi wake.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Yahwe anatazama kutoka mbinguni; yeye huona watu wote.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Kutokea mahali ambapo yeye anaishi, huwatazama wote waishio juu ya nchi.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Yeye anaye iumba mioyo yao na kuyaona matendo yao yote.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Hakuna mfalme anayeokolewa na jeshi kubwa; shujaa haokolewi na nguvu zake nyingi.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Farasi sio salama kwa ajili ya ushindi; ijapokuwa nguvu zake ni nyingi, hawezi kuokoa.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Tazama, macho ya Yahwe yako kwa wale wanao mhofu yeye, wale wanao litumainia agano lake takatifu
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
kuwaokoa maisha yao na mauti na kuwaweka hai wakati wa jaa.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Sisi tunamngoja Yahwe, yeye ni msaada wetu na ngao yetu.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Mioyo yetu hufurahia ndani yake, kwa kuwa tunaamini katika jina lake takatifu.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Yahwe, agano lako takatifu, liwe pamoja nasi tuwekapo tumaini letu katika wewe.