< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Mwimbieni Bwana kwa furaha, enyi wenye haki; kusifu kunawapasa wanyofu wa moyo.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Msifuni Bwana kwa kinubi, mwimbieni sifa kwa zeze la nyuzi kumi.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Mwimbieni wimbo mpya; pigeni kwa ustadi, na mpaze sauti za shangwe.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Maana neno la Bwana ni haki na kweli, ni mwaminifu kwa yote atendayo.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Bwana hupenda uadilifu na haki; dunia imejaa upendo wake usiokoma.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Kwa neno la Bwana mbingu ziliumbwa, jeshi lao la angani kwa pumzi ya kinywa chake.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Ameyakusanya maji ya bahari kama kwenye chungu; vilindi vya bahari ameviweka katika ghala.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Dunia yote na imwogope Bwana, watu wote wa dunia wamche.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Kwa maana Mungu alisema, na ikawa, aliamuru na ikasimama imara.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Bwana huzuia mipango ya mataifa, hupinga makusudi ya mataifa.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Lakini mipango ya Bwana inasimama imara milele, makusudi ya moyo wake kwa vizazi vyote.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Heri taifa ambalo Bwana ni Mungu wao, watu ambao aliwachagua kuwa urithi wake.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Kutoka mbinguni Bwana hutazama chini na kuwaona wanadamu wote;
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
kutoka maskani mwake huwaangalia wote wakaao duniani:
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
yeye ambaye huumba mioyo yao wote, ambaye huangalia kila kitu wanachokitenda.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Hakuna mfalme aokokaye kwa ukubwa wa jeshi lake; hakuna shujaa aokokaye kwa wingi wa nguvu zake.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Farasi ni tumaini la bure kwa wokovu, licha ya nguvu zake nyingi, hawezi kuokoa.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Lakini macho ya Bwana yako kwa wale wamchao, kwa wale tumaini lao liko katika upendo wake usio na kikomo,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
ili awaokoe na mauti, na kuwahifadhi wakati wa njaa.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Sisi tunamngojea Bwana kwa matumaini, yeye ni msaada wetu na ngao yetu.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Mioyo yetu humshangilia, kwa maana tunalitumainia jina lake takatifu.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Upendo wako usio na mwisho ukae juu yetu, Ee Bwana, tunapoliweka tumaini letu kwako.

< Zabura 33 >