< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
ALEGRAOS, justos, en Jehová: á los rectos es hermosa la alabanza.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Celebrad á Jehová con arpa: cantadle con salterio y decacordio.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Cantadle canción nueva: hacedlo bien tañendo con júbilo.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Porque recta es la palabra de Jehová, y toda su obra con verdad [hecha].
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
El ama justicia y juicio: de la misericordia de Jehová está llena la tierra.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Por la palabra de Jehová fueron hechos los cielos, y todo el ejército de ellos por el espíritu de su boca.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
El junta como en un montón las aguas de la mar: él pone en depósitos los abismos.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Tema á Jehová toda la tierra: teman de él todos los habitadores del mundo.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Porque él dijo, y fué hecho; él mandó, y existió.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Jehová hace nulo el consejo de las gentes, y frustra las maquinaciones de los pueblos.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
El consejo de Jehová permanecerá para siempre; los pensamientos de su corazón por todas las generaciones.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Bienaventurada la gente de que Jehová es su Dios; el pueblo á quien escogió por heredad para sí.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Desde los cielos miró Jehová; vió á todos los hijos de los hombres:
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Desde la morada de su asiento miró sobre todos los moradores de la tierra.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
El formó el corazón de todos ellos; él considera todas sus obras.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
El rey no es salvo con la multitud del ejército: no escapa el valiente por la mucha fuerza.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Vanidad es el caballo para salvarse: por la grandeza de su fuerza no librará.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
He aquí, el ojo de Jehová sobre los que le temen, sobre los que esperan en su misericordia;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Para librar sus almas de la muerte, y para darles vida en el hambre.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Nuestra alma esperó á Jehová; nuestra ayuda y nuestro escudo es él.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Por tanto en él se alegrará nuestro corazón, porque en su santo nombre hemos confiado.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Sea tu misericordia, oh Jehová, sobre nosotros, como esperamos en ti.

< Zabura 33 >