< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Cantád justos en Jehová: a los rectos es hermosa la alabanza.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Celebrád a Jehová con arpa: con salterio y decacordio cantád a él.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Cantád a él canción nueva: hacéd bien tañendo con júbilo.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Porque derecha es la palabra de Jehová: y toda su obra con verdad.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Él ama justicia y juicio: de la misericordia de Jehová está llena la tierra.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Con la palabra de Jehová fueron hechos los cielos: y con el espíritu de su boca todo el ejército de ellos.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
El junta, como en un montón, las aguas de la mar: él pone por tesoros los abismos.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Teman a Jehová toda la tierra: teman de él todos los habitadores del mundo.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Porque él dijo, y fue; él mandó y estuvo.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Jehová hace anular el consejo de las gentes, y él hace anular las maquinaciones de los pueblos.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
El consejo de Jehová permanecerá para siempre; los pensamientos de su corazón, por generación y generación.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Bienaventurada la gente a quien Jehová es su Dios: el pueblo a quien escogió por heredad para sí.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Desde los cielos miró Jehová; vio a todos los hijos de Adam.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Desde la morada de su asiento miró sobre todos los moradores de la tierra.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
El formó el corazón de todos ellos; él entiende todas sus obras.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
El rey no es salvo con la multitud del ejército; el valiente no escapa con la mucha fuerza.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Vanidad es el caballo para la salud; con la multitud de su fuerza no escapa.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
He aquí, el ojo de Jehová sobre los que le temen; sobre los que esperan su misericordia;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Para librar de la muerte a sus almas; y para darles vida en la hambre.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Nuestra alma esperó a Jehová; nuestro ayudador y nuestro escudo es él.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Por tanto en él se alegrará nuestro corazón, porque en su santo nombre hemos confiado.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Sea tu misericordia, o! Jehová, sobre nosotros, como te hemos esperado.