< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
¡Que los rectos griten de alegría! ¡Que te adoren los que hacen el bien!
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Alaba al Señor con Lira, toca música para él con el decacordio.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Cántale nueva canción; toca bien tus instrumentos y grita de alegría.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Porque la palabra del Señor es verdadera, y él merece toda la confianza en lo que hace.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Él ama todo lo bueno y lo correcto; la tierra está llena del amor inefable del Señor.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
El Señor habló y los cielos fueron hechos. Su boca sopló, y todas las estrellas existieron.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Reúne las aguas de los mares, mantiene almacenadas las profundidades del océano.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Reverencie toda la tierra al Señor; que todos los habitantes de la tierra se maravillen con su presencia.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Porque él habló, y el mundo vino a la existencia; dio la orden, y fue creado.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
El Señor frustra los planes de las naciones y de los pueblos.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Pero el plan del Señor permanece para siempre. Sus propósitos perduran a través de las generaciones.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Feliz es la nación cuyo Dios es el Señor, el pueblo que ha escogido como enteramente suyo.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
El Señor mira desde los cielos y ve toda la humanidad,
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
desde su trono él ve a todos los que habitan en la tierra.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Él creó sus mentes, y reconoce todo lo que hacen.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Ni el más grande ejército puede salvar a un rey; ni la fuerza más poderosa puede salvar a un guerrero.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
No te engañes: un caballo de guerra no puede darte la victoria, ni su increíble fuerza podrá salvarte.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
El Señor cuida de quienes lo siguen con reverencia, de los que depositan su esperanza en su amor inagotable,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
para que los salve de la muerte y para que los mantenga vivos cuando el hambre ataque.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Ponemos nuestra confianza en el Señor. Él es nuestra ayuda y nuestro defensor.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Nuestros corazones están llenos de alegría, porque confiamos en su carácter santo.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Que tu gran amor descanse sobre nosotros mientras esperamos en ti.

< Zabura 33 >