< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Prepevajte, pravični v Gospodu, poštenim se spodobi hvalno petje.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Slavite Gospoda sè strunami, s citrami in desetostrunjem mu pojte.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Pojte mu novo pesem, krepko bijte na strune, da doni.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Ker prava je beseda Gospodova; in stanovitno vse delo njegovo.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Pravico ljubi in sodbo; milosti Gospodove polna je zemlja.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Z besedo Gospodovo ustvarjena so nebesa, in z dihom ust njegovih vsa vojska nebeška.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Morske vode znaša kakor kup in v shrambe deva valove.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Gospoda naj se bojé vse dežele, pred njim naj trepetajo vsi sveta prebivalci.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Ker na besedo njegovo je, karkoli je, na zapoved njegovo postane.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Gospod uničuje narodov sklep, misli ljudstev podira.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Sklep pa Gospodov ostane vekomaj, misli srca njegovega od roda do roda.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Blagor narodu, katerega Bog je Gospod, ljudstvo, katero si je izvolil v last.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Z nebes gleda Gospod, vidi vse sinove človeške.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Z mesta prebivališča svojega gleda dol na vse zemlje prebivalce.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
In obrazovatelj tudi njih src, pazi na vsa njihova dela.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Ni ga kralja, da bi se rešil z množico krdél; mogočni se ne otme z množico moči.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Goljufiv je konj za rešitev in z množico moči svoje ne oprosti jezdeca.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Glej, oko Gospodovo pazi na nje, kateri se ga bojé, na njé, kateri čakajo milosti njegove;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Da reši smrti njih dušo, in jih žive ohrani v lakoti.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Duša naša čaka Gospoda; pomoč je naša in ščit naš.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Ker v njem se raduje srce naše, kajti zaupamo njegovemu svetemu imenu.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Milost tvoja, Gospod, bodi nad nami, kakor te pričakujemo.

< Zabura 33 >