< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Fagna dykk høgt i Herren, de rettferdige! For de trurøkne sømer seg lovsong.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Prisa Herren med strengeleik, lovsyng honom til tistrengja harpa!
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Syng honom ein ny song, rør strengen fagert med fagnadljod.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
For Herrens ord er ærleg meint, og all hans gjerning er trufast.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Han elskar rettferd og rett; av Herrens nåde er jordi full.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Himlarne er skapte ved Herrens ord, og all deira her ved hans munns ande.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Han samlar havsens vatn som ei muga, legg dei djupe vatn i upplagshus.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
All jordi må ottast for Herren, for honom ræddast alle som bur i mannheimen.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
For han tala, og so vart det; han baud, og so stod det der.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Herren spiller heidningefolks råd, gjer folkeslags tankar til inkjes.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Herrens råd stend ved lag i all æva, hans hjartans tankar frå ætt til ætt.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Sælt er det folk som hev Herren til sin Gud, det folk som han valde ut til sin arv.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Frå himmelen skodar Herren ned, han ser alle menneskjeborni.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Frå den staden der han bur, ser han ned til alle som bur på jordi,
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
han som lagar deira hjarto alle saman, han som merkar alle deira gjerningar.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Ein konge vert ikkje frelst ved sin store styrke, ei kjempa ikkje berga ved si store kraft.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Hesten er sviksam hjelp til frelsa, og med sin store styrke bergar han ikkje.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Sjå, Herrens auga ser til deim som ottast honom, som ventar på hans nåde
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
til å fria deira sjæl frå dauden og halda deim i live i hungersnaud.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Vår sjæl stundar på Herren; han er vår hjelp og vår skjold.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
For i honom gled vårt hjarta seg, for me set vår lit til hans heilage namn.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Di nåde, Herre, vere yver oss, so som me vonar på deg!

< Zabura 33 >