< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Bino bato ya sembo, bobeta milolo ya esengo na tina na Yawe! Kokumisa Nzambe ebongi na bato oyo bazali alima.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Bosanzola Yawe na nzenze, bosanzola Ye na lindanda ya basinga zomi.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Boyembela Yawe nzembo ya sika, bobetisa bibetelo mindule elongo na koganga ya esengo.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Pamba te Liloba na Yawe ezali alima, misala na Ye nyonso ekokisamaka na boyengebene.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Yawe alingaka bosembo mpe alima; mokili etondi na bolingo na Ye.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Likolo ekelamaki na Liloba na Yawe; mampinga na yango nyonso, na nzela ya pema ya monoko na Ye.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Asangisaka mayi ya bibale minene esika moko, mpe atiaka yango na bisika ya mozindo.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Tika ete mokili mobimba etosa Yawe! Tika ete bavandi nyonso ya mokili balenga liboso na Ye.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Pamba te alobaki, mpe likambo esalemaki; mpe apesaki mitindo, mpe emonanaki.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Yawe akweyisaka mikano ya bikolo, abebisaka mabongisi ya bato.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Kasi mikano ya Yawe etikalaka mpo na seko, mabongisi ya motema na Ye, mpo na bikeke nyonso.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Esengo na ekolo oyo Yawe azali Nzambe na yango. Esengo na bato oyo aponaki mpo na libula na Ye.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Yawe atalaka wuta na likolo, amonaka bana nyonso ya bato.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Wuta na evandelo na Ye, atalaka bavandi nyonso ya mokili.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Ye oyo asalaka mitema nyonso ya bato asosolaka makambo nyonso oyo basalaka.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Ezali te limpinga monene nde ebikisaka mokonzi to nguya monene nde ekangolaka elombe.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Mpunda ezali na nguya te ya kopesa lobiko, makasi na yango nyonso ekangolaka te.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Nzokande Yawe atalaka bato oyo batosaka Ye, ba-oyo batiaka elikya na bolingo kati na Ye,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
mpo na kokangola bango na kufa mpe kobatela bango na bomoi ata na tango ya nzala makasi.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Totielaka Yawe motema; azali lisungi mpe nguba na biso.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Solo, mitema na biso esepelaka kati na Ye, pamba te totiaka elikya na biso kati na Kombo na Ye ya bule.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Yawe, lokola totiaka elikya na biso kati na Yo, tika ete bolingo na Yo ezala elongo na biso.

< Zabura 33 >