< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Hai orang-orang saleh, bersoraklah gembira karena apa yang telah dilakukan TUHAN; patutlah orang jujur memuji-muji.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Bersyukurlah kepada TUHAN dengan kecapi, bernyanyilah bagi-Nya dengan iringan musik.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Nyanyikanlah lagu baru bagi TUHAN, mainkan kecapi baik-baik dan bersoraklah dengan riang!
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Semua perkataan TUHAN dapat dipercaya; Ia setia dalam segala perbuatan-Nya.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Ia mencintai kejujuran dan keadilan; seluruh bumi penuh dengan kasih-Nya.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
TUHAN memberi perintah, maka langit tercipta; matahari, bulan dan bintang dijadikan oleh sabda-Nya.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Semua air laut dikumpulkan-Nya di suatu tempat, samudra raya ditahan-Nya di dalam bendungan.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Biarlah seluruh bumi takut kepada TUHAN dan penduduk dunia menghormati Dia.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Sebab Ia bersabda, lalu semuanya dijadikan; Ia memberi perintah, maka semuanya ada.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
TUHAN menggagalkan rencana bangsa-bangsa, Ia meniadakan niat mereka.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Tetapi rencana TUHAN tetap bertahan, rancangan-Nya teguh sepanjang zaman.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Berbahagialah bangsa yang mengakui TUHAN sebagai Allahnya, berbahagialah umat yang dipilih-Nya menjadi milik-Nya!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Dari surga TUHAN memandang ke bawah, dan Ia melihat seluruh umat manusia.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Dari takhta-Nya TUHAN mengamati semua yang mendiami bumi.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Dialah yang membentuk hati mereka, dan tahu segala perbuatan mereka.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Raja tidak menang karena besarnya tentara, prajurit tidak selamat karena kekuatannya.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Kuda tak dapat diandalkan untuk menang, kekuatannya yang besar tak dapat menyelamatkan.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
TUHAN menjaga orang-orang yang takwa yang mengharapkan kasih-Nya.
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Ia menyelamatkan mereka dari maut, dan menghidupi mereka di masa kelaparan.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Maka kita berharap kepada TUHAN, Dialah penolong dan pembela kita.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Kita bersukaria karena Dia dan percaya kepada nama-Nya yang suci.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Semoga kami tetap Kaukasihi, ya TUHAN, sebab kami berharap kepada-Mu.