< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Lobpreiset Jehovah, ihr Gerechten, den Redlichen ziemet das Lob.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Bekennt mit der Harfe den Jehovah, mit zehnsaitigem Psalter singet Ihm Psalmen.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Singt Ihm ein neues Lied, macht es gut mit Spielen im Jubelsang.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Denn gerade ist Jehovahs Wort, und all Sein Tun in Wahrheit.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Er liebt Gerechtigkeit und Gericht, der Barmherzigkeit Jehovahs ist die Erde voll.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Die Himmel sind gemacht durch Jehovahs Wort, und vom Hauche Seines Mundes all ihr Heer.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Er faßt zusammen wie in einen Haufen des Meeres Wasser, Er gibt die Tiefen in Schatzkammern.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Es fürchte sich vor Jehovah all die Erde; vor Ihm sei bange allen, die in der Welt wohnen.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Denn Er spricht, und es geschieht; Er gebeut, und es steht da.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Jehovah macht zunichte den Rat der Völkerschaften, stößt um die Gedanken der Völker.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Jehovahs Ratschluß steht in Ewigkeit, die Gedanken Seines Herzens für Geschlecht und Geschlecht.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Selig die Völkerschaft, deren Gott Jehovah ist, das Volk, das Er Sich zum Erbe hat erwählt.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Vom Himmel blickt Jehovah, Er sieht alle Söhne des Menschen.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Von der Wohnstätte Seines Sitzes erschaut Er alle, so auf Erden wohnen.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Der ihr Herz bildet zumal, Der merkt auf all ihr Tun.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Dem König hilft nicht seine viele Streitmacht; der Held wird nicht errettet durch die viele Kraft.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Lug ist des Rosses Heil und durch seine viele Kraft läßt es nicht entrinnen.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Siehe, Jehovahs Auge ist auf denen, so Ihn fürchten, die auf Seine Barmherzigkeit warten.
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Daß ihre Seele Er vom Tod errette und sie am Leben erhalte in der Hungersnot.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Unsere Seele wartet auf Jehovah, unser Beistand und unser Schild ist Er.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Denn in Ihm ist fröhlich unser Herz, denn wir vertrauen auf den Namen Seiner Heiligkeit.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Jehovah, Deine Barmherzigkeit sei über uns, wie wir Deiner warten.

< Zabura 33 >