< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Jauchzet dem HERRN, ihr Gerechten! Den Redlichen ziemt Lobgesang.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Preiset den HERRN mit der Harfe, spielet ihm auf dem zehnsaitigen Psalter;
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
singet ihm ein neues Lied, spielet gut, mit Posaunenschall!
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Denn das Wort des HERRN ist richtig, und all sein Werk ist Treue.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Er liebt Gerechtigkeit und Gericht; die Erde ist voll der Gnade des HERRN.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Die Himmel sind durch das Wort des HERRN gemacht und ihr ganzes Heer durch den Geist seines Mundes.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Er türmt die Meereswellen auf und sammelt Wasservorräte an.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Alle Welt fürchte den HERRN, und vor ihm scheue sich alles, was auf dem Erdboden wohnt.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Denn er sprach, und es geschah; er gebot, und es stand da!
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Der HERR vereitelt den Rat der Heiden, er verhindert die Anschläge der Völker.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Der Rat des HERRN besteht ewiglich, seines Herzens Gedanken für und für.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Wohl dem Volk, dessen Gott der HERR ist, dem Volk, das er sich zum Erbe erwählt hat!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Vom Himmel schaut der HERR herab, er betrachtet alle Menschenkinder;
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
von seinem festen Thron sieht er alle, die auf Erden wohnen;
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
er, der ihrer aller Herz gebildet hat, bemerkt auch alle ihre Werke.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Einem König ist nicht geholfen mit viel Heeresmacht, ein Held wird nicht errettet durch große Kraft;
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
das Roß ist unzuverlässig zur Rettung, und trotz seiner großen Stärke kann man nicht entrinnen.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Siehe, der HERR hat ein Auge auf die, so ihn fürchten, die auf seine Gnade hoffen,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
daß er ihre Seele vom Tode errette und sie in der Teuerung am Leben erhalte.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Unsre Seele harrt auf den HERRN; er ist unsre Hilfe und unser Schild.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Ja, an ihm soll unser Herz sich freuen; denn auf seinen heiligen Namen haben wir unser Vertrauen gesetzt.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Deine Gnade, o HERR, sei über uns, wie wir es von dir erhoffen!

< Zabura 33 >