< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Justes, exultez dans le Seigneur, aux cœurs droits convient sa louange.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Louez le Seigneur sur la harpe: jouez pour lui du psaltérion à dix cordes.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Chantez-lui un cantique nouveau: par un heureux concert, jouez pour lui du psaltérion, au milieu des acclamations.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Parce que la parole du Seigneur est droite, et que toutes ses œuvres sont conformes à la fidélité dans les promesses.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Il aime la miséricorde et la justice: la terre est remplie de sa miséricorde.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
La parole du Seigneur a affermi les cieux: et du souffle de sa bouche, vient toute leur vertu.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Il rassemble comme dans une outre les eaux de la mer: il renferme comme dans des trésors les abîmes.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Que toute la terre craigne le Seigneur: qu’à sa présence aussi soient émus tous ceux qui habitent l’univers.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Car il a dit, et les choses ont été faites: il a commandé, et elles ont été créées.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Le Seigneur dissipe les conseils des nations; il réprouve aussi les pensées des peuples, et il réprouve les conseils des princes.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Mais le conseil du Seigneur demeure éternellement: les pensées de son cœur dans toutes les générations.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Bienheureuse la nation dont le Seigneur est le Dieu! Bienheureux le peuple qu’il a choisi pour son héritage!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Du haut du ciel, le Seigneur a regardé: il a vu tous les enfants des hommes.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
De la demeure qu’il s’est préparée, il a porté ses regards sur tous ceux qui habitent la terre.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
C’est lui qui a formé un à un leurs cœurs; lui connaît toutes leurs œuvres.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Un roi ne se sauve point par sa grande puissance, et un géant ne se sauvera point par la grandeur de sa force.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Le cheval est un espoir trompeur de salut: toute sa force ne le sauvera point.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Voilà que les yeux du Seigneur sont sur ceux qui le craignent, et sur ceux qui espèrent en sa miséricorde,
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Afin de délivrer leurs âmes de la mort, et de les nourrir dans la famine.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Notre âme attend avec constance le Seigneur, parce qu’il est notre aide et notre protecteur;
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Parce que c’est en lui que se réjouira notre cœur, et que c’est en son saint nom que nous avons espéré.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Que votre miséricorde, Seigneur, soit sur nous, selon que nous avons espéré en vous

< Zabura 33 >