< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Vous justes, chantez de joie à cause de l'Eternel; sa louange est bienséante aux hommes droits.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Célébrez l'Eternel avec le violon, chantez-lui des Psaumes avec la musette, et l'instrument à dix cordes.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Chantez-lui un nouveau Cantique, touchez adroitement [vos instruments de musique] avec un cri de réjouissance.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Car la parole de l'Eternel est pure, et toutes ses œuvres sont avec fermeté.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Il aime la justice et la droiture; la terre est remplie de la gratuité de l'Eternel.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Les cieux ont été faits par la parole de l'Eternel, et toute leur armée par le souffle de sa bouche.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Il assemble les eaux de la mer comme en un monceau, il met les abîmes [comme] dans des céliers.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Que toute la terre craigne l'Eternel, que tous les habitants de la terre habitable le redoutent.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Car il a dit, et [ce qu'il a dit] a eu son être, il a commandé, et la chose a comparu.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
L'Eternel dissipe le conseil des nations, il anéantit les desseins des peuples;
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
[Mais] le conseil de l'Eternel se soutient à toujours; les desseins de son cœur subsistent d'âge en âge.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Ô! que bienheureuse est la nation dont l'Eternel est le Dieu, [et] le peuple qu'il s'est choisi pour héritage!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
L'Eternel regarde des Cieux, il voit tous les enfants des hommes.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Il prend garde du lieu de sa résidence à tous les habitants de la terre.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
C'est lui qui forme également leur cœur, et qui prend garde à toutes leurs actions.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Le Roi n'est point sauvé par une grosse armée, et l'homme puissant n'échappe point par [sa] grande force.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Le cheval manque à sauver, et ne délivre point par la grandeur de sa force.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Voici, l'œil de l'Eternel est sur ceux qui le craignent, sur ceux qui s'attendent à sa gratuité.
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Afin qu'il les délivre de la mort, et les entretienne en vie durant la famine.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Notre âme s'est confiée en l'Eternel; il est notre aide et notre bouclier.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Certainement notre cœur se réjouira en lui, parce que nous avons mis notre assurance en son saint Nom.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Que ta gratuité soit sur nous, ô Eternel! selon que nous nous sommes confiés en toi