< Zabura 33 >
1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
De David. Justes, mettez votre joie dans le Seigneur; la louange convient aux cœurs droits.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Chantez sur la cithare les louanges du Seigneur; chantez pour lui sur la harpe à dix cordes.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Chantez pour lui un cantique nouveau; chantez en accord et à haute voix.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Car la parole du Seigneur est sûre; il est fidèle en toutes ses œuvres.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Il aime la miséricorde et la justice; la terre est pleine de la miséricorde du Seigneur.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Les cieux se sont affermis à la parole du Seigneur, et toute leur vertu au souffle de sa bouche.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Il a rassemblé comme dans une outre les eaux de la mer; il a déposé les abîmes dans ses trésors.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Que toute la terre craigne le Seigneur; que ceux qui habitent le monde tremblent devant lui.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Car il a dit, et ils ont été; il a commandé, et ils ont été créés.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
Le Seigneur dissipe les conseils des nations; il réprouve les pensées des peuples; il réprouve les desseins des princes.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Mais le conseil du Seigneur dure éternellement; les pensées de son cœur vivent de génération en génération.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Heureuse la nation dont le Seigneur est le Dieu; heureux le peuple qu'il s'est choisi pour héritage.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Le Seigneur a regardé du ciel, il a vu tous les fils des hommes.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
De la demeure qu'il s'est préparée, il regarde tous ceux qui habitent la terre.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
C'est lui qui a formé le cœur de chacun d'eux; il connaît toutes leurs œuvres.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Un roi n'est pas sauvé par une armée nombreuse; un géant ne sera pas délivré par sa grande force.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Le cheval trompe celui qui en attend le salut, et la multitude de ses forces ne le sauvera point.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Voilà que les yeux du Seigneur sont sur ceux qui le craignent et qui espèrent en sa miséricorde;
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Pour qu'il sauve leurs âmes de la mort, qu'il les nourrisse au temps de la famine.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Notre âme attend le Seigneur; car il est notre protecteur et notre champion;
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Car en lui notre cœur mettra sa joie, et nous avons espéré en son saint nom.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Seigneur, répands sur nous ta miséricorde, autant que nous l'avons espéré de toi.