< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Be joyful, O ye righteous, in the Lord; [for] unto the righteous praise is comely.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Give thanks unto the Lord with the harp: with the ten-stringed psaltery do ye sing [praises] unto him.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Sing unto him a new song; play beautifully amidst a triumphant shout.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
For the word of the Lord is upright; and all his works [are done] in truth.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
He loveth righteousness and justice: the earth is full of the kindness of the Lord.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
By the word of the Lord were the heavens made; and by the breath of his mouth all their host.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
He gathereth together like heaps the waters of the sea: he layeth up in store-houses the depths [of the sea].
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Let all the earth fear the Lord: of him stand in awe all the inhabitants of the world.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
For he spoke, and it came into being: he commanded, and it stood fast.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
The Lord frustrateth the resolves of the nations: he bringeth to nought the thoughts of the people.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
The counsel of the Lord will stand for ever, the thoughts of his heart from generation to generation.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Happy is the nation whose God is the Lord, the people whom he hath chosen for himself as a heritage.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
The Lord looketh from heaven; he seeth all the sons of men.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
From the place of his habitation he directeth his view upon all the inhabitants of the earth;
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
He fashioneth their hearts altogether; he hath regard to all their works.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
The king is not saved by the multitude of an army: a mighty man is not delivered by much strength.
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Vain is the horse for victory: nor shall he deliver any by the greatness of his strength.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Behold, the eye of the Lord is upon those that fear him, upon those that hope for his kindness.
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
To deliver from death their soul, and to keep them alive in famine.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Our soul waiteth for the Lord: our help and our shield is he.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
For in him shall our heart rejoice: because in his holy name have we trusted.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Let thy kindness, O Lord, be upon us, even as we hope in thee.

< Zabura 33 >