< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Gij rechtvaardigen! zingt vrolijk in den HEERE; lof betaamt den oprechten.
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Looft den HEERE met de harp; psalmzingt Hem met de luit, en het tiensnarig instrument.
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Zingt Hem een nieuw lied; speelt wel met vrolijk geschal.
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Want des HEEREN woord is recht, en al Zijn werk getrouw.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Hij heeft gerechtigheid en gericht lief; de aarde is vol van de goedertierenheid des HEEREN.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Door het Woord des HEEREN zijn de hemelen gemaakt, en door den Geest Zijns monds al hun heir.
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Hij vergadert de wateren der zee als op een hoop; Hij stelt den afgronden schatkameren.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Laat de ganse aarde voor den HEERE vrezen; laat alle inwoners van de wereld voor Hem schrikken.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Want Hij spreekt, en het is er; Hij gebiedt, en het staat er.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
De HEERE vernietigt den raad der heidenen; Hij breekt de gedachten der volken.
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Maar de raad des HEEREN bestaat in eeuwigheid, de gedachten Zijns harten van geslacht tot geslacht.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Welgelukzalig is het volk, welks God de HEERE is; het volk, dat Hij Zich ten erve verkoren heeft.
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
De HEERE schouwt uit den hemel, en ziet alle mensenkinderen.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Hij ziet uit van Zijn vaste woonplaats op alle inwoners der aarde.
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Hij formeert hun aller hart; Hij let op al hun werken.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Een koning wordt niet behouden door een groot heir; een held wordt niet gered door grote kracht;
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Het paard feilt ter overwinning, en bevrijdt niet door zijn grote sterkte.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Ziet, des HEEREN oog is over degenen, die Hem vrezen, op degenen, die op Zijn goedertierenheid hopen.
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Om hun ziel van den dood te redden, en om hen bij het leven te houden in den honger.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Onze ziel verbeidt den HEERE: Hij is onze Hulp en ons Schild.
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
Want ons hart is in Hem verblijd, omdat wij op den Naam Zijner heiligheid vertrouwen.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Uw goedertierenheid, HEERE! zij over ons; gelijk als wij op U hopen.

< Zabura 33 >