< Zabura 33 >

1 Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
Gij rechtvaardigen, heft Jahweh een jubelzang aan; De psalm is een lust voor de vromen!
2 Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
Looft Jahweh met citers, Bespeelt voor Hem de tiensnarige harp;
3 Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
Stemt een nieuw lied voor Hem aan, Tokkelt de lieren, lustig en luid!
4 Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
Want Jahweh’s woord is waarachtig, Onveranderlijk al zijn daden.
5 Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
Gerechtigheid en recht heeft Hij lief; Van Jahweh’s goedheid is de aarde vol.
6 Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
Door het woord van Jahweh zijn de hemelen gemaakt, Door de adem van zijn mond heel hun heir;
7 Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
Hij verzamelde het water der zee in een zak, Legde de oceanen in schuren op.
8 Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
Heel de aarde moet Jahweh vrezen, Al de bewoners der wereld Hem duchten.
9 Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
Want Hij sprak: en het was; Hij gebood: en het stond.
10 Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
De raadslagen der volken gooit Jahweh omver, Hij verijdelt de plannen der naties;
11 Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
Maar Jahweh’s raadsbesluit staat in eeuwigheid vast: Wat zijn hart heeft bedacht, van geslacht tot geslacht.
12 Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
Gelukkig de natie, die Jahweh tot God heeft, Het volk, dat Hij Zich tot erfdeel verkoos!
13 Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
Jahweh ziet neer uit de hemel, Richt zijn blik op alle kinderen der mensen.
14 daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
Hij let van de plaats, waar Hij troont, Op alle bewoners der aarde:
15 shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
Hij, die aller hart heeft geschapen, En al hun daden doorgrondt.
16 Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
Geen koning overwint door de macht van zijn heir, Geen held wordt gered door geweldige kracht;
17 Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
Ook het ros kan de zege niet schenken, Door zijn grote snelheid niet redden.
18 Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
Maar het oog van Jahweh rust op hen, die Hem vrezen, En die op zijn goedheid vertrouwen:
19 don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
Om ze te redden van de dood, Ze in het leven te houden bij hongersnood.
20 Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
Onze ziel blijft opzien tot Jahweh: Hij is onze hulp en ons schild;
21 A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
In Hem verheugt zich ons hart, Wij vertrouwen op zijn heilige Naam.
22 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.
Uw genade, o Jahweh, dale over ons neer, Naarmate wij op U blijven hopen!

< Zabura 33 >