< Zabura 32 >
1 Ta Dawuda. Maskil ne. Mai farin ciki ne shi wanda aka gafarta masa laifofinsa, wanda aka shafe zunubansa.
(Af David. En maskil.) Salig den, hvis Overtrædselse er forladt, hvis Synd er skjult;
2 Mai farin ciki ne mutumin da Ubangiji ba ya lissafin zunubinsa a kansa wanda kuma babu ruɗu a ruhunsa.
saligt det Menneske, HERREN ej tilregner Skyld, og i hvis Ånd der ikke er Svig.
3 Sa’ad da na yi shiru, ƙasusuwana sun yi ta mutuwa cikin nishina dukan yini.
Mine Ben svandt hen, så længe jeg tav, under Jamren Dagen igennem,
4 Gama dare da rana hannunka yana da nauyi a kaina; an shanye ƙarfina ƙaf sai ka ce a zafin bazara. (Sela)
thi din Hånd lå tungt på mig både Dag og Nat, min Livskraft svandt som i Sommerens Tørke. (Sela)
5 Sa’an nan na furta zunubina a gare ka ban kuwa ɓoye laifina ba. Na ce, “Zan furta laifofina ga Ubangiji.” Ka kuwa gafarta laifin zunubina. (Sela)
Min Synd bekendte jeg for dig, dulgte ikke min Skyld; jeg sagde: "Mine Overtrædelser vil jeg bekende for HERREN!" Da tilgav du mig min Syndeskyld. (Sela)
6 Saboda haka bari duk mai tsoron Allah yă yi addu’a gare ka yayinda kake samuwa; tabbatacce sa’ad da manyan ruwaye suka taso, ba za su kai wurinsa ba.
Derfor bede hver from til dig, den Stund du findes. Kommer da store Vandskyl, ham skal de ikke nå.
7 Kai ne wurin ɓuyata; za ka tsare ni daga wahala ka kewaye ni da waƙoƙin ceto. (Sela)
Du er mit Skjul, du frier mig af Trængsel, med Frelsesjubel omgiver du mig. (Sela)
8 Zan umarce ka in kuma koyar da kai a hanyar da za ka bi; Zan ba ka shawara in kuma lura da kai.
Jeg vil lære dig og vise dig, hvor du skal gå, jeg vil råde dig ved at fæste mit Øje på dig.
9 Kada ka zama kamar doki ko doki, wanda ba su da azanci wanda dole sai an bi da su da linzami da ragama in ba haka ba, ba za su zo wurinka ba.
Vær ikke uden Forstand som Hest eller Muldyr, der tvinges med Tømme og Bidsel, når de ikke vil komme til dig.
10 Azaban mugu da yawa suke, amma ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa kan kewaye mutumin da ya dogara gare shi.
Den gudløses Smerter er mange, men den, der stoler på HERREN, omgiver han med Nåde.
11 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji ku kuma yi murna, ku adalai; ku rera, dukanku waɗanda zuciyarku take daidai!
Glæd jer i HERREN, I retfærdige, fryd jer, jubler, alle I oprigtige af Hjertet!