< Zabura 31 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
Načelniku godbe, psalm Davidov. K tebi, Gospod, pribegam, naj se ne osramotim vekomaj; s pravico svojo osvobodi me.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Nagni mi uho svoje, hitro me reši; močna skala mi bodi, trden grad, da se rešim.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
Ker skala moja si in trdnjava moja, torej zavoljo imena svojega vodi me in spremljaj me.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
Izpelji me iz mreže, katero so skrili zoper mene: ker ti si moja moč.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
V roko tvojo izročam svoj duh; otél si me, Gospod, Bog mogočni, resnični.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
Sovražim nje, ki česté ničemurnosti prazne; ker jaz zaupam v Gospoda,
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
Da se bodem radoval in veselil dobrote tvoje, ko se bodeš ozrl v siromaštvo moje, spoznal duše moje stiske,
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
In ne izdal me sovražniku v roko, na široko postavil noge moje.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Milost mi stórí, Gospod, ker v stiski sem; od žalovanja hira oko moje, duša moja in telo moje.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
Ker od žalosti peša življenje moje in leta moja od zdihovanja; od kazni krivice, katero trpim, hira krepost moja; in kosti moje ginejo.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
Pri vseh sovražnikih svojih sem v sramoto, in pri sosedih svojih jako, in strah znancem svojim; zagledavši me zunaj bežé od mene.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
V pozabljenje me zagrebava srce, kakor mrtvega; jaz sem kakor orodje potrto.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
Ker zasramovanje čujem od mnogih, strah okrog in okrog; posvetujoč se vkup zoper mene mislijo, kako bi prestregli dušo mojo.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
Jaz pa v té zaupam, Gospod, govoreč: Bog si moj;
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
V rokah tvojih so časi moji; potegni me iz rok sovražnikov mojih in njih, ki me preganjajo.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Daj, da sveti obličje tvoje nad tvojim hlapcem; reši me po milosti svoji.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
Gospod, naj se ne osramotim, ker te kličem; osramoté se naj krivični, pogubé se v grob. (Sheol h7585)
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Neme naj postanejo ustne lažnjive, katere govoré zoper pravičnega trdó, z napuhom in zaničevanjem.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
Kako obila je dobrota tvoja, katero hraniš njim, ki te česté; izkazuješ njim, ki pribegajo k tebi pred sinovi človeškimi!
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
Skrivaš jih v skrivališči pričujočnosti svoje pred móž napuhom; skrivaš jih v koči pred prepirom jezikov.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Blagoslovljen Gospod, ker mi izkazuje čudovito milost svojo; stavi me kakor v trdno mesto.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
Jaz sem bil sicer rekel v naglici svoji; Iztrebljen sem izpred tvojih oči; vendar si slišal molitev mojih glas, ko semi vpil k tebi.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Ljubite Gospoda vsi, katerim izkazuje dobroto; Gospoda, ki varuje zveste, in povrača preobilno, dela reči veličastne.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Potolažite se, in pokrepčal bode srce vaše, vsi, ki upate v Gospoda.

< Zabura 31 >