< Zabura 31 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
Em ti, Senhor, confio; nunca me deixes confundido: livra-me pela tua justiça.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Inclina para mim os teus ouvidos, livra-me depressa; sê a minha firme rocha, uma casa fortíssima que me salve.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
Porque tu és a minha rocha e a minha fortaleza; pelo que, por amor do teu nome, guia-me e encaminha-me.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
Tira-me da rede que para mim esconderam, pois tu és a minha força.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
Nas tuas mãos encomendo o meu espírito: tu me redimiste, Senhor Deus da verdade.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
Aborreço aqueles que se entregam a vaidades enganosas; eu porém confio no Senhor.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
Eu me alegrarei e regozijarei na tua benignidade, pois consideraste a minha aflição: conheceste a minha alma nas angústias.
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
E não me entregaste nas mãos do inimigo; puseste os meus pés num lugar espaçoso.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Tem misericórdia de mim, ó Senhor, porque estou angustiado: consumidos estão de tristeza os meus olhos, a minha alma e o meu ventre.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
Porque a minha vida está gasta de tristeza, e os meus anos de suspiros; a minha força descai por causa da minha iniquidade, e os meus ossos se consomem.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
Fui opróbrio entre todos os meus inimigos, até entre os meus vizinhos, e horror para os meus conhecidos: os que me viam na rua fugiam de mim.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
Estou esquecido no coração deles, como um morto; sou como um vaso quebrado.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
Pois ouvi a murmuração de muitos, temor havia ao redor; enquanto juntamente consultavam contra mim, intentaram tirar-me a vida.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
Mas eu confiei em ti, Senhor: e disse: Tu és o meu Deus.
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
Os meus tempos estão nas tuas mãos: livra-me das mãos dos meus inimigos e dos que me perseguem.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Faze resplandecer o teu rosto sobre o teu servo: salva-me por tuas misericórdias.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
Não me deixes confundido, Senhor, porque te tenho invocado: deixa confundidos os ímpios, e emudeçam na sepultura. (Sheol h7585)
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Emudeçam os lábios mentirosos que falam coisas más com soberba e desprezo contra o justo.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
Oh! quão grande é a tua bondade, que guardaste para os que te temem! a qual obraste para aqueles que em ti confiam na presença dos filhos dos homens!
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
Tu os esconderás, no secreto da tua presença, dos desaforos dos homens: encobri-los-ás em um pavilhão da contenda das línguas.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Bendito seja o Senhor, pois fez maravilhosa a sua misericórdia para comigo em cidade segura.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
Pois eu dizia na minha pressa: Estou cortado de diante dos teus olhos; não obstante, tu ouviste a voz das minhas suplicas, quando eu a ti clamei.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Amai ao Senhor, vós todos que sois seus santos; porque o Senhor guarda os fieis e retribui com abundância ao que usa de soberba.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Esforçai-vos, e ele fortalecerá o vosso coração, vós todos que esperais no Senhor.

< Zabura 31 >