< Zabura 31 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
Pour le chef musicien. Un psaume de David. En toi, Yahvé, je trouve refuge. Que je ne sois jamais déçu. Délivre-moi dans ta justice.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Inclinez votre oreille vers moi. Délivrez-moi rapidement. Sois pour moi un rocher solide, une maison de défense pour me sauver.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
Car tu es mon rocher et ma forteresse, c'est pourquoi, pour l'amour de ton nom, conduis-moi et guide-moi.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
arrache-moi du filet qu'ils ont tendu pour moi, car tu es ma forteresse.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
Entre tes mains, je remets mon esprit. Tu me rachètes, Yahvé, Dieu de vérité.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
Je déteste ceux qui considèrent les vanités mensongères, mais je me confie à Yahvé.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
Je me réjouirai et me réjouirai de ta bonté, car tu as vu ma détresse. Tu as connu mon âme dans l'adversité.
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
Tu ne m'as pas livré aux mains de l'ennemi. Tu as mis mes pieds dans un grand endroit.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Aie pitié de moi, Yahvé, car je suis dans la détresse. Mon œil, mon âme et mon corps se décomposent avec le chagrin.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
Car ma vie se passe dans la tristesse, mes années avec des soupirs. Ma force faiblit à cause de mon iniquité. Mes os ont dépéri.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
A cause de tous mes adversaires, je suis devenu complètement méprisable pour mes voisins, une horreur pour mes connaissances. Ceux qui m'ont vu dans la rue m'ont fui.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
Je suis oublié de leur cœur comme un mort. Je suis comme une poterie cassée.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
Car j'ai entendu la calomnie de beaucoup, la terreur de tous côtés, alors qu'ils conspirent ensemble contre moi, ils complotent pour m'enlever la vie.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
Mais moi, j'ai confiance en toi, Yahvé. J'ai dit: « Tu es mon Dieu. »
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
Mes temps sont dans ta main. Délivre-moi de la main de mes ennemis et de ceux qui me persécutent.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Fais briller ton visage sur ton serviteur. Sauve-moi dans ta bonté.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
Que je ne sois pas déçu, Yahvé, car j'ai fait appel à toi. Que les méchants soient déçus. Qu'ils se taisent dans le séjour des morts. (Sheol h7585)
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Que les lèvres menteuses soient muettes, qui parlent contre les justes avec insolence, avec orgueil et mépris.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
Oh, comme ta bonté est grande, que tu as mis en réserve pour ceux qui te craignent, que tu as mis en œuvre pour ceux qui se réfugient en toi, devant les fils des hommes!
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
Dans l'abri de ta présence, tu les protégeras des complots de l'homme. Tu les garderas secrètement dans une demeure, loin des querelles de langues.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Loué soit Yahvé, car il m'a montré sa merveilleuse bonté dans une ville forte.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
Quant à moi, j'ai dit dans ma précipitation: « Je suis retranché de devant vos yeux. » Cependant, vous avez entendu la voix de mes demandes lorsque je criais vers vous.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Oh, aimez Yahvé, vous tous ses saints! Yahvé préserve les fidèles, et rétribue pleinement celui qui se comporte avec arrogance.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Sois fort, et que ton cœur prenne courage, vous tous qui espérez en Yahvé.

< Zabura 31 >