< Zabura 31 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
To the chief Musician, A Psalm of David. In thee, O LORD, do I put my trust; let me never be ashamed: deliver me in thy righteousness.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Bow down thy ear to me; deliver me speedily: be thou my strong rock, for a house of defense to save me.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
For thou [art] my rock and my fortress; therefore for thy name's sake lead me, and guide me.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
Pull me out of the net that they have laid privily for me: for thou [art] my strength.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
Into thy hand I commit my spirit: thou hast redeemed me, O LORD God of truth.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
I have hated them that regard lying vanities: but I trust in the LORD.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
I will be glad and rejoice in thy mercy: for thou hast considered my trouble; thou hast known my soul in adversities;
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
And hast not shut me up into the hand of the enemy: thou hast set my foot in a large room.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Have mercy upon me, O LORD, for I am in trouble: my eye is consumed with grief, [yes], my soul and my belly.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
For my life is spent with grief, and my years with sighing: my strength faileth because of my iniquity, and my bones are consumed.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
I was a reproach among all my enemies, but especially among my neighbors, and a fear to my acquaintance: they that saw me without fled from me.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
I am forgotten as a dead man out of mind: I am like a broken vessel.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
For I have heard the slander of many: fear [was] on every side: while they took counsel together against me, they devised to take away my life.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
But I trusted in thee, O LORD: I said, Thou [art] my God.
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
My times [are] in thy hand: deliver me from the hand of my enemies, and from them that persecute me.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Make thy face to shine upon thy servant: save me for thy mercies' sake.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol h7585)
Let me not be ashamed, O LORD; for I have called upon thee: let the wicked be ashamed, and let them be silent in the grave. (Sheol h7585)
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Let the lying lips be put to silence; which speak grievous things proudly and contemptuously against the righteous.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
[Oh] how great [is] thy goodness, which thou hast laid up for them that fear thee; [which] thou hast wrought for them that trust in thee before the sons of men!
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
Thou shalt hide them in the secret of thy presence from the pride of man: thou shalt keep them secretly in a pavilion from the strife of tongues.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Blessed [be] the LORD: for he hath showed me his wonderful kindness in a strong city.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
For I said in my haste, I am cut off from before thy eyes: nevertheless thou heardest the voice of my supplications when I cried to thee.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
O love the LORD, all ye his saints: [for] the LORD preserveth the faithful, and plentifully rewardeth the proud doer.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Be of good courage, and he will strengthen your heart, all ye that hope in the LORD.

< Zabura 31 >