< Zabura 31 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
For the leader. A psalm of David. In you, O Lord, I take refuge; let me never be put to shame. Rescue me in your faithfulness;
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
incline to me your ear. Deliver me speedily. Be to me a rock of defence, a fortified house, to save me.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
For my rock and my fortress are you; lead me and guide me so your name will be honored.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
Draw me out of the net they have hid for me, for you yourself are my refuge.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
Into your hand I commend my spirit: you ransom me, Lord, faithful God.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
I hate those devoted to worthless idols; I trust in the Lord.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
I will rejoice and be glad in your love, because you have looked on my misery, and cared for me in my distress.
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
You have not given me into the enemy’s hand, you have set my feet in a spacious place.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Be gracious to me, Lord, for I am distressed; my eye is wasted away with sorrow.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
For my life is consumed with grief, and my years with sighing. My strength is broken with misery, my bones waste away.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
The scorn of all my foes, the butt of my neighbors am I, a terror to my acquaintance. At the sight of me in the street people turn quickly away.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
I am clean forgotten like the dead, am become like a ruined vessel.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
I hear the whispers of many – terror on every side – scheming together against me, plotting to take my life.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
But my trust is in you, Lord. “You are my God,” I say;
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
my times are in your hand, save me from the hand of the foes who pursue me.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Make your face to shine on your servant, save me in your love.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol )
Put me not, O Lord, to shame, for I have called upon you. Let the wicked be put to shame silent in Sheol. (Sheol )
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
Strike the false lips dumb, that speak proudly against the righteous with haughtiness and contempt.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
How great is the goodness you have treasured for those who fear you, and wrought for those who take refuge in you, in plain sight of all!
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
In your sheltering wings you hide them from plottings of people, you keep them safe in a bower from the chiding of tongues.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Blest be the Lord for the wonderful love he has shown me in time of distress.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
For I had said in panic, “I am driven clean out of your sight.” But you heard my plea, when I cried to you for help.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Love the Lord, all you faithful; the Lord protects the loyal, but repays the haughty in full.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Let your hearts be courageous and strong, all you who wait on the Lord.