< Zabura 31 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka bari in taɓa shan kunya; ka cece ni cikin rahamarka.
Unto the end. A Psalm of David according to an ecstasy. In you, Lord, I have hoped; let me never be confounded. In your justice, deliver me.
2 Ka juye kunnenka gare ni, ka zo da sauri ka cece ni; ka zama dutsen mafakata, mafaka mai ƙarfi na cetona.
Incline your ear to me. Hasten to rescue me. Be for me a protector God and a house of refuge, so as to accomplish my salvation.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata, saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
For you are my strength and my refuge; and for the sake of your name, you will lead me and nourish me.
4 Ka’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini, gama kai ne mafakata.
You will lead me out of this snare, which they have hidden for me. For you are my protector.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna; ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.
Into your hands, I commend my spirit. You have redeemed me, O Lord, God of truth.
6 Na ƙi waɗanda suke manne wa gumakan banza; na dogara ga Ubangiji.
You have hated those who practice emptiness to no purpose. But I have hoped in the Lord.
7 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikin ƙaunarka, gama ka ga azabata ka kuma san wahalar raina.
I will exult and rejoice in your mercy. For you have looked upon my humility; you have saved my soul from needfulness.
8 Ba ka ba da ni ga abokin gāba ba amma ka sa ƙafafuna a wuri mai sarari.
And you have not enclosed me in the hands of the enemy. You have set my feet in a spacious place.
9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama ina cikin damuwa; idanuna sun gaji da baƙin ciki, raina da jikina sun tafke tilis.
Have mercy on me, Lord, for I am troubled. My eye has been disturbed by wrath, along with my soul and my gut.
10 Baƙin ciki ya rufe raina shekaruna sun cika da nishi; ƙarfina ya karai saboda azaba, ƙasusuwana kuma sun gaji tiƙis.
For my life has fallen into sorrow, and my years into sighing. My virtue has been weakened in poverty, and my bones have been disturbed.
11 Saboda dukan abokan gābana, Na zama tamƙar abin reni na maƙwabtana; na zama abin tsoro ga abokaina, waɗanda suka gan ni a titi sukan gudu daga gare ni.
I have become a disgrace among all my enemies, and even more so to my neighbors, and a dread to my acquaintances. Those who catch sight of me, flee away from me.
12 An manta da ni sai ka ce na mutu; na zama kamar fasasshen kasko.
I have become forgotten, like one dead to the heart. I have become like a damaged utensil.
13 Gama nakan ji raɗe-raɗen mutane masu yawa; akwai tsoro a kowane gefe; suna ƙulla maƙarƙashiya a kaina suna shirya su ɗauke raina.
For I have heard the harsh criticism of many who linger in the area. While assembled together against me in that place, they deliberated on how to take away my life.
14 Amma na dogara gare ka, ya Ubangiji; na ce, “Kai ne Allahna.”
But I have hoped in you, O Lord. I said, “You are my God.”
15 Lokutana suna a hannuwanka; ka cece ni daga abokan gābana da kuma daga waɗanda suke fafara ta.
My fate is in your hands. Rescue me from the hand of my enemies and from those who are persecuting me.
16 Bari fuskarka ta haskaka a kan bawanka; ka cece ni da ƙaunarka marar ƙarewa.
Shine your face upon your servant. Save me in your mercy.
17 Kada ka bari in sha kunya, ya Ubangiji, gama na yi kuka gare ka; amma bari mugaye su sha kunya su kuma kwanta shiru a cikin kabari. (Sheol )
Do not let me be confounded, Lord, for I have called upon you. Let the impious be ashamed and be drawn down into Hell. (Sheol )
18 Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
May deceitful lips be silenced: those that speak iniquity against the just, in arrogance and in abusiveness.
19 Alherinka da girma yake, wanda ka ajiye domin waɗanda suke tsoronka, wanda ka mayar a gaban mutane a kan waɗanda suke neman mafaka daga gare ka.
How great is the multitude of your sweetness, O Lord, which you keep hidden for those who fear you, which you have perfected for those who hope in you, in the sight of the sons of men.
20 Cikin inuwar kasancewarka ka ɓoye su daga makircin mutane; a wurin zamanka ka kiyaye su lafiya daga harsuna masu zagi.
You hide them in the concealment of your face, from the disturbance of men. You protect them in your tabernacle, from the contradiction of tongues.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya nuna ƙaunarsa mai banmamaki gare ni sa’ad da aka yi mini kwanto kewaye da birni.
Blessed is the Lord. For he has shown his wonderful mercy to me, in a fortified city.
22 Cikin tsorona na ce, “An yanke ni daga gabanka!” Duk da haka ka ji kukata na neman jinƙai sa’ad da na kira gare ka don taimako.
But I said in the excess of my mind: “I have been cast away from the glance of your eyes.” And so, you heeded the voice of my prayer, while I was still crying out to you.
23 Ku ƙaunaci Ubangiji, dukanku tsarkakansa! Ubangiji yakan adana amintattu, amma masu girman kai yakan sāka musu cikakke.
Love the Lord, all you his saints. For the Lord will require truth, and he will abundantly repay those who act with arrogance.
24 Ku yi ƙarfin hali ku kuma ƙarfafa, dukanku masu sa bege a kan Ubangiji.
Act manfully, and let your heart be strengthened, all you who hope in the Lord.