< Zabura 30 >

1 Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
Un salmo. Un Canto para la Dedicación del Templo. Por David. Te ensalzaré, Yahvé, porque me has levantado, y no has hecho que mis enemigos se alegren de mí.
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
Yahvé, mi Dios, a ti clamé, y tú me has curado.
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
Yahvé, has sacado mi alma del Seol. Me has mantenido con vida, para que no baje a la fosa. (Sheol h7585)
4 Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
Canten alabanzas a Yahvé, santos suyos. Da gracias a su santo nombre.
5 Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
Porque su cólera no es más que un momento. Su favor es para toda la vida. El llanto puede permanecer durante la noche, pero la alegría llega por la mañana.
6 Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
En cuanto a mí, dije en mi prosperidad, “Nunca seré movido”.
7 Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
Tú, Yahvé, cuando me favoreciste, hiciste que mi montaña se mantuviera firme; pero cuando ocultaste tu rostro, me preocupé.
8 A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
A ti, Yahvé, te clamé. Hice una súplica al Señor:
9 “Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
“¿Qué provecho hay en mi destrucción, si desciendo a la fosa? ¿Te alabará el polvo? ¿Declarará su verdad?
10 Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
Escucha, Yahvé, y ten piedad de mí. Yahvé, sé mi ayudante”.
11 Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
Tú has convertido mi luto en una danza para mí. Me has quitado el cilicio y me has vestido de alegría,
12 don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.
para que mi corazón te cante alabanzas y no calle. Yahvé, mi Dios, te daré gracias por siempre.

< Zabura 30 >