< Zabura 30 >

1 Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
Mazmur Daud. Nyanyian untuk peresmian Rumah Allah. Aku memuji Engkau, ya TUHAN, sebab Engkau sudah menyelamatkan aku dan tidak membiarkan musuhku menyoraki aku.
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
TUHAN Allahku, aku berseru kepada-Mu minta tolong, dan Engkau menyembuhkan aku.
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
Engkau meluputkan aku dari alam maut, dan menghidupkan aku dari antara orang-orang mati. (Sheol h7585)
4 Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
Nyanyikanlah puji-pujian bagi TUHAN, hai umat-Nya yang setia, dan bersyukurlah kepada Yang Mahasuci.
5 Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
Sebab sebentar saja TUHAN marah, kebaikan-Nya berlangsung seumur hidup. Di waktu malam aku menangis, tetapi fajar membawa kegembiraan.
6 Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
Waktu merasa aman, aku berkata, "Aku tak akan dikalahkan!"
7 Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
Sebab Engkau baik hati kepadaku, ya TUHAN, Kaujadikan aku seperti gunung yang kuat. Tetapi kemudian Engkau bersembunyi daripadaku, dan aku menjadi takut.
8 A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
Kepada-Mu, ya TUHAN, aku berseru, kepada TUHAN aku memohon,
9 “Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
"Apa gunanya bagi-Mu jika aku mati dan turun ke liang kubur? Mungkinkah orang mati memuji Engkau dan mewartakan kesetiaan-Mu?
10 Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
Dengarlah, ya TUHAN, dan kasihanilah aku. TUHAN tolonglah aku!"
11 Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
Ratapanku telah Kauubah menjadi tarian gembira, Kauambil kesedihanku dan Kaupenuhi aku dengan sukacita.
12 don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.
Maka aku tak mau berdiam diri; kunyanyikan pujian bagi-Mu, ya TUHAN Allahku, dan bersyukur kepada-Mu untuk selama-lamanya!

< Zabura 30 >