< Zabura 30 >

1 Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
מזמור שיר-חנכת הבית לדוד ב ארוממך יהוה כי דליתני ולא-שמחת איבי לי
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
יהוה אלהי-- שועתי אליך ותרפאני
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
יהוה--העלית מן-שאול נפשי חייתני מיורדי- (מירדי-) בור (Sheol h7585)
4 Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
זמרו ליהוה חסידיו והודו לזכר קדשו
5 Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
כי רגע באפו-- חיים ברצונו בערב ילין בכי ולבקר רנה
6 Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
ואני אמרתי בשלוי-- בל-אמוט לעולם
7 Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
יהוה-- ברצונך העמדתה להררי-עז הסתרת פניך הייתי נבהל
8 A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
אליך יהוה אקרא ואל-אדני אתחנן
9 “Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
מה-בצע בדמי ברדתי אל-שחת היודך עפר היגיד אמתך
10 Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
שמע-יהוה וחנני יהוה היה-עזר לי
11 Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
הפכת מספדי למחול לי פתחת שקי ותאזרני שמחה
12 don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.
למען יזמרך כבוד-- ולא ידם יהוה אלהי לעולם אודך

< Zabura 30 >