< Zabura 30 >

1 Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
“A psalm of David. To the air of songs for the dedication of a house.” I will extol thee, O LORD! for thou hast lifted me up, And hast not suffered my enemies to rejoice over me.
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
O Jehovah, my God! I called upon thee, and thou hast healed me!
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
O LORD! thou hast raised me up from the underworld; Thou hast kept me alive, that I should not go down to the pit. (Sheol h7585)
4 Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
Sing unto the LORD, O ye his servants! And praise his holy name!
5 Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
For his anger endureth but a moment, But his favor through life; In the evening sorrow may be a guest, But joy cometh in the morning.
6 Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
I said in my prosperity, “I shall never be moved!”
7 Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
Thou, O LORD! by thy favor, hast made my mountain to stand strong; Thou didst hide thy face, and I was troubled!
8 A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
I cried unto thee, O LORD! To the LORD I made supplication:
9 “Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
“What will my blood profit thee, that I should go down to the pit? Can dust praise thee? Can it declare thy faithfulness?
10 Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
Hear, O LORD! and have pity upon me! Be thou, LORD! my helper!”
11 Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
Thou didst turn my mourning into dancing; Thou didst loose my sackcloth, and gird me with gladness.
12 don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.
Therefore I will sing praise to thee, and not be silent. O Jehovah, my God! I will give thanks to thee for ever!

< Zabura 30 >