< Zabura 30 >

1 Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
A psalm of David. A psalm for the dedication of the Temple. I want to tell everyone how good you are, Lord, for you saved me, and you didn't let my enemies triumph over me.
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
Lord, my God, I called out to you for help, and you have healed me.
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
Lord, you rescued me from the grave, you brought me back to life, saving me from going down into the pit of death. (Sheol h7585)
4 Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
You who trust the Lord, sing praises to him, and be thankful for his holy character!
5 Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
For his anger only lasts a moment, but his favor lasts a lifetime. You may spend the night in tears, but happiness comes with the morning.
6 Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
When things were going well, I said, “Nothing will ever shake me!”
7 Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
Lord, when you showed me your favor I stood as strong as a mountain; when you turned away from me I was terrified.
8 A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
I called out to you for help, Lord. I asked the Lord for grace, saying,
9 “Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
What would you gain if I die, if I go down into the pit of death? Would my dust praise you? Would it tell of your trustworthiness?
10 Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
Please listen to me, Lord, and be gracious to me! Lord, you are the one who helps me.
11 Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
You have turned my weeping into dancing. You have taken off my clothes of sackcloth and dressed me in happiness,
12 don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.
so I can sing praises to you and not keep quiet. Lord my God, I will thank you forever!

< Zabura 30 >