< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Señor, ¡cuánto aumentan quienes me atacan! en gran número vienen contra mí.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Son innumerables los que dicen de mi alma, no hay ayuda para él en Dios. (Selah)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Pero tú, oh Señor, eres escudo, estás a mi alrededor, tú eres mi gloria y el que levanta mi cabeza.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
Clamó a gritos al Señor con mi voz, y él me responde desde su santo monte. (Selah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Me acuesto y duermo tranquilo, y otra vez estaba despierto; porque el Señor me sustentaba.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
No temeré, aunque diez mil vinieron contra mí, y pusieren sitio contra mí.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
¡Levántate Señor! ¡mantenme a salvo, oh mi Dios! porque tú has dado todos mis enemigos en sus mejillas; los dientes de los malvados han sido quebrantados por ti.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
La salvación viene del Señor; tu bendición está en tu pueblo. (Selah)

< Zabura 3 >