< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Господе! Како је много непријатеља мојих! Многи устају на ме.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Многи говоре за душу моју: Нема му помоћи од Бога.
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Али Ти си, Господе, штит који ме заклања, слава моја; Ти подижеш главу моју.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
Гласом својим вичем ка Господу, и чује ме са свете горе своје.
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Ја лежем, спавам и устајем, јер ме Господ чува.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
Не бојим се много хиљада народа што са свих страна наваљује на ме.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Устани, Господе! Помози ми, Боже мој! Јер Ти удараш по образу све непријатеље моје; разбијаш зубе безбожницима.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Од Господа је спасење; нека буде на народу Твом благослов Твој!

< Zabura 3 >