< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
En salme av David, da han flydde for Absalom, sin sønn. Herre, hvor mange mine fiender er! Mange reiser sig imot mig.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Mange sier til min sjel: Det er ingen frelse for ham hos Gud. (Sela)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Men du, Herre, er et skjold omkring mig, min ære og den som opløfter mitt hode!
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
Høit ropte jeg til Herren, og han svarte mig fra sitt hellige berg. (Sela)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Jeg la mig og sov inn, jeg våknet; for Herren støtter mig.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
Jeg frykter ikke for titusener av folk, som har lagt sig mot mig rundt omkring.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Reis dig, Herre, frels mig, min Gud! For du har slått alle mine fiender på kinnbenet, du har sønderbrutt de ugudeliges tenner.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Herren hører frelsen til; over ditt folk være din velsignelse! (Sela)

< Zabura 3 >