< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
ダビデその子アブサロムを避しときのうた ヱホバよ我にあたする者のいかに蔓延れるや 我にさからびて起りたつもの多し
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
わが霊魂をあげつらひて かれは神にすくはるることなしといふ者ぞおほき (セラ)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
されどヱホバよ なんぢは我をかこめる盾わが榮わが首をもたげ給ふものなり
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
われ聲をあげてヱホバによばはればその聖山より我にこたへたまふ (セラ)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
われ臥していね また目さめたり ヱホバわれを支へたまへばなり
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
われをかこみて立かまへたる干萬の人をも我はおそれじ
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
ヱホバよねがはくは起たまへ わが神よわれを救ひたまへ なんぢ曩にわがすべての仇の頬骨をうち惡きものの歯ををりたまへり
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
救はヱホバにあり ねがはくは恩恵なんぢの民のうへに在んことを (セラ)

< Zabura 3 >