< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Éternel, que mes ennemis sont nombreux! Combien de gens se lèvent contre moi!
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Combien, qui disent de mon âme: Point de salut pour lui auprès de Dieu! (Sélah, pause)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Mais toi, Éternel, tu es mon bouclier, ma gloire, et celui qui me fait lever la tête.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
Je crie de ma voix à l'Éternel, et il me répond de sa montagne sainte. (Sélah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Je me couche, je m'endors, et je me réveille; car l'Éternel me soutient.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
Je ne crains point les milliers d'hommes qui se rangent de toute part contre moi.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Lève-toi, Éternel, sauve-moi, mon Dieu! Car tu as frappé à la joue tous mes ennemis, tu as brisé les dents des méchants.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Le salut vient de l'Éternel; ta bénédiction est sur ton peuple! (Sélah)

< Zabura 3 >