< Zabura 3 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Chant de David. A l’occasion de sa fuite devant Absalon, son fils Yahweh, que mes ennemis sont nombreux! Quelle multitude se lève contre moi!
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Nombreux sont ceux qui disent à mon sujet: « Plus de salut pour lui auprès de Dieu! » — Séla.
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Mais toi, Yahweh, tu es mon bouclier; tu es ma gloire, et tu relèves ma tête.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
De ma voix je crie vers Yahweh, et il me répond de sa montagne sainte. — Séla.
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Je me suis couché et me suis endormi; je me suis réveillé, car Yahweh est mon soutien.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
je ne crains pas devant le peuple innombrable, qui m’assiège de toutes parts.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Lève-toi, Yahweh! Sauve-moi, mon Dieu! Car tu frappes à la joue tous mes ennemis, tu brises les dents des méchants.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
A Yahweh le salut! Que ta bénédiction soit sur ton peuple! — Séla.