< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Yahweh, I have many enemies [DOU]! There are many people who oppose/rebel against me.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many people are saying about me, “God will [certainly] not help him!”
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But Yahweh, you are like a shield [that protects me] [MET]. You greatly honor me, and you encourage me (OR, enable me to triumph over my enemies) [IDM].
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
I cry out to you, Yahweh, and you answer me from [Zion], your sacred hill.
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
[At night] I lie down and sleep, and I awake [in the morning feeling good/refreshed] because you, Yahweh, (take care of/protect) me [all during the night].
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
There may be thousands of [enemy] soldiers who surround me, but I am not afraid.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Yahweh, arise! My God, [come and] rescue me [again]! You [insult] my enemies by slapping them on their cheeks; [when you strike them], you break their teeth, [with the result that they cannot hurt anyone] [MET].
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Yahweh, you are the one who saves your people [from their enemies]. Yahweh, bless your people!

< Zabura 3 >