< Zabura 3 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Lord, how are they increased that trouble me! many are they that rise up against me.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many there be which say of my soul, There is no help for him in God. (Selah)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But you, O LORD, are a shield for me; my glory, and the lifter up of my head.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
I cried to the LORD with my voice, and he heard me out of his holy hill. (Selah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
I laid me down and slept; I awaked; for the LORD sustained me.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
I will not be afraid of ten thousands of people, that have set themselves against me round about.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Arise, O LORD; save me, O my God: for you have smitten all my enemies on the cheek bone; you have broken the teeth of the ungodly.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Salvation belongs to the LORD: your blessing is on your people. (Selah)