< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
A Psalm of David, when he fled from his son Absalom. O LORD, how my foes have increased! How many rise up against me!
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many say of me, “God will not deliver him.”
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But You, O LORD, are a shield around me, my glory, and the One who lifts my head.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
To the LORD I cry aloud, and He answers me from His holy mountain.
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
I lie down and sleep; I wake again, for the LORD sustains me.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
I will not fear the myriads set against me on every side.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Arise, O LORD! Save me, O my God! Strike all my enemies on the jaw; break the teeth of the wicked.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Salvation belongs to the LORD; may Your blessing be on Your people.

< Zabura 3 >