< Zabura 3 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Jehovah, how my adversaries are increased! Many are those who rise up against me.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many there are who say of my soul, There is no help for him in God. (Selah)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But thou, O Jehovah, are a shield about me, my glory and he who lifts up of my head.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
I cry to Jehovah with my voice, and he answers me out of his holy hill. (Selah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
I laid down and slept. I awoke, for Jehovah sustains me.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
I will not be afraid of ten thousands of the people who have set themselves against me round about.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Arise, O Jehovah. Save me, O my God. For thou have smitten all my enemies upon the cheek bone. Thou have broken the teeth of the wicked.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Salvation belongs to Jehovah. Thy blessing be upon thy people. (Selah)