< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
Een psalm van David, bij zijn vlucht voor zijn zoon Absalom. Jahweh, hoe talrijk zijn mijn belagers, Hoe talrijk, die tegen mij opstaan;
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Hoe velen, die van mij zeggen: Voor hem geen heil bij zijn God!
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
Toch zijt Gij, Jahweh, het schild dat mij dekt, Mijn glorie en trots!
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
Ik behoef maar tot Jahweh te roepen, Dan verhoort Hij mij van zijn heilige berg.
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
Ik leg mij neer, slaap rustig in, Ontwaak, want Jahweh beschut mij.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
Zo vrees ik de duizenden niet, Die van alle kant mij omringen.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Sta op dan, Jahweh; Red mij, mijn God! Want Gij slaat al mijn vijanden in het gezicht, Stoot de bozen hun tanden stuk.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Bij U, Jahweh, is redding; Op uw volk rust uw zegen.

< Zabura 3 >