< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Dawid dwom. Momfa mma Awurade no, mo ɔsoro abɔde, momfa anuonyam ne tumi mma Awurade.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Momfa anuonyam a ɛfata Awurade din mma no; monsɔre Awurade wɔ nʼanuonyam kronkron mu.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Awurade nne wɔ nsu no so; anuonyam Nyankopɔn bobɔ mu, Awurade bobɔ mu wɔ nsu akɛse so.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Awurade nne mu wɔ tumi; Awurade nne mu wɔ anuonyam.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Awurade nne bubu sida; Awurade nne bubu Lebanon sida mu nketenkete
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Ɔma Lebanon huruhuruw te sɛ nantwi ba, na Sirion nso sɛ ɛko ba.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Awurade nne pa ma anyinam gya dɛw.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Awurade nne wosow sare so; Awurade wosow Kades sare.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Awurade nne kyinkyim adum na ɛma kwae yɛ kwaterekwa. Nʼasɔredan mufo nyinaa teɛ mu ka se, “Anuonyam nka Onyankopɔn!”
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Awurade di hene wɔ nsuyiri so; wɔasi Awurade hene afebɔɔ.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Awurade ma ne nkurɔfo ahoɔden, na ɔde asomdwoe hyira wɔn.

< Zabura 29 >