< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Dar al Señor, seres celestiales, dar al Señor gloria y poder.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Dar a Jehová toda la gloria de su nombre; darle culto en la hermosura de la santidad.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
La voz del Señor está sobre las aguas; el Dios de gloria truena; el Señor sobre el mar inmenso.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
La voz del Señor está llena de poder; la voz del Señor tiene un sonido imponente.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Por la voz del Señor están los cedros quebrantados, los cedros del Líbano son quebrantados por el Señor.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Los hace saltar como becerros; Al Líbano y al Sirión como hijos de búfalos.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
A la voz del Señor se ven llamas de fuego.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
A la voz del Señor se estremece el desierto, y se sacude el desierto de Cades.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
A la voz del Señor las encinas las desgaja, las hojas son arrancadas de los árboles: en su Templo todos le rinden honor.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
El Señor tenía su trono como rey cuando las aguas vinieron sobre la tierra; el Señor está sentado como rey para siempre.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
El Señor dará fortaleza a su pueblo; el Señor dará a su pueblo la bendición de la paz.

< Zabura 29 >