< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
¡Tributen a Yavé, oh hijos de los poderosos! ¡Tributen a Yavé la gloria y el poder!
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
¡Tributen a Yavé la gloria debida a su Nombre! ¡Póstrense ante Yavé en el esplendor de la santidad!
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Voz de Yavé sobre las aguas: ¡El ʼElohim de gloria truena! ¡Yavé está sobre muchas aguas!
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Voz de Yavé es poderosa, Voz de Yavé es majestuosa.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Voz de Yavé que quiebra los cedros, Yavé destroza los cedros del Líbano.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Él hace saltar al Líbano como un becerro.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Voz de Yavé que enciende llamaradas.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Voz de Yavé que estremece el desierto. Yavé sacude al desierto de Cades.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Voz de Yavé que estremece los robles y desnuda los bosques. En su Templo todos proclaman su gloria.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Yavé preside en el diluvio. Yavé se sienta como Rey para siempre.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Yavé dará fortaleza a su pueblo. Yavé bendecirá a su pueblo con paz.

< Zabura 29 >