< Zabura 29 >
1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Un Salmo de David. Honren al Señor, hijos de Dios, honren su gloria y su poder.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Honren al Señor por su glorioso carácter, inclínense con reverencia al Señor en su majestuosa santidad.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
La voz del Señor se escucha sobre los mares. El Dios de gloria truena. Los truenos del Señor se escuchan sobre el vasto océano.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
La voz del Señor es poderosa; la voz del Señor es majestuosa;
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
la voz del Señor destruye los cedros, incluso rompe los cedros del Líbano.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Hace que las montañas del Líbano salten como un ternero, y el monte Hermon como un joven buey salvaje.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
La voz del Señor resplandece como rayos de luz.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
La voz del Señor causa terremotos en el desierto; el desierto de Kadesh tiembla.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
La voz del Señor hace que la cierva embarazada entre en labores de parto; desnuda los bosques. En su Templo todos los adoradores cantan, “¡Gloria!”
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
El Señor se sienta en su trono sobre las aguas tormentosas; el Señor es el Rey eternal.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
El Señor le da fuerza a su pueblo; el Señor los bendice con paz.