< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
مزمور داوود. ای فرشتگان، خداوند را ستایش کنید! شکوه و عظمت او را بستایید!
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
خداوند را به خاطر جلال نامش بپرستید. خداوند را در شکوه قدوسیتش پرستش کنید.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
صدای خداوند از فراز دریاها شنیده می‌شود؛ او همچون رعد می‌غرد! صدای او بر اقیانوسها طنین‌افکن است!
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
صدای خداوند پرقدرت و باشکوه است.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
صدای خداوند درختان سِدر را می‌شکند. خداوند درختان سِدر لبنان را خُرد می‌کند.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
او کوههای لبنان را می‌لرزاند و کوه حرمون را مانند گوساله به جست و خیز وا می‌دارد.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
صدای خداوند رعد و برق ایجاد می‌کند،
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
دشتها را به لرزه در می‌آورد و صحرای قادش را می‌جنباند.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
صدای خداوند درخت بلوط را می‌لرزاند و برگهای درختان جنگل را به زمین می‌ریزد. در خانهٔ خداوند، همه جلال و عظمت او را می‌ستایند.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
خداوند بر آبهای عمیق فرمان می‌راند و تا به ابد سلطنت می‌نماید.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
خداوند به قوم برگزیدهٔ خود قدرت می‌بخشد و صلح و سلامتی نصیب ایشان می‌کند.

< Zabura 29 >