< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
مزمور داود ای فرزندان خدا، خداوند را توصیف کنید. جلال و قوت را برای خداوندتوصیف نمایید.۱
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
خداوند را به جلال اسم اوتمجید نمایید. خداوند را در زینت قدوسیت سجده کنید.۲
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
آواز خداوند فوق آبها است. خدای جلال رعد می‌دهد. خداوند بالای آبهای بسیار است.۳
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
آواز خداوند با قوت است. آوازخداوند با جلال است.۴
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
آواز خداوند سروهای آزاد را می‌شکند. خداوند سروهای آزاد لبنان رامی شکند.۵
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
آنها را مثل گوساله می‌جهاند. لبنان وسریون را مثل بچه گاو وحشی.۶
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
آواز خداوندزبانه های آتش را می‌شکافد.۷
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
آواز خداوندصحرا را متزلزل می‌سازد. خداوند صحرای قادش را متزلزل می‌سازد.۸
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
آواز خداوند غزالهارا به درد زه می‌اندازد، و جنگل را بی‌برگ می‌گرداند. و در هیکل او جمیع جلال را ذکرمی کنند.۹
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
خداوند بر طوفان جلوس نموده. خداوند نشسته است پادشاه تا ابدالاباد.۱۰
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
خداوند قوم خود را قوت خواهد بخشید. خداوند قوم خود را به سلامتی مبارک خواهدنمود.۱۱

< Zabura 29 >