< Zabura 29 >
1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Inikeni iNkosi, lina madodana abalamandla, inikeni iNkosi udumo lamandla.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Inikeni iNkosi udumo lwebizo layo, likhothame eNkosini ebuhleni bobungcwele.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Ilizwi leNkosi liphezu kwamanzi; uNkulunkulu wenkazimulo uyaduma; iNkosi iphezu kwamanzi amanengi.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Ilizwi leNkosi lilamandla, ilizwi leNkosi lilobukhosi.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Ilizwi leNkosi lephula imisedari, yebo, iNkosi yephula imisedari yeLebhanoni.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Yenza yona-ke iqolotshe njengethole, iLebhanoni leSiriyoni njengethole lenyathi.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Ilizwi leNkosi lidabula amalangabi omlilo.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Ilizwi leNkosi lizamazamisa inkangala, iNkosi izamazamisa inkangala yeKadeshi.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Ilizwi leNkosi lizalisa izimpala, lihlubule amahlathi; lethempelini layo konke kuthi: Udumo.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
UJehova uhlezi phezu kukazamcolo, yebo, uJehova uhlezi eyiNkosi kuze kube nininini.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
INkosi izanika abantu bayo amandla; iNkosi ibusise abantu bayo ngokuthula.