< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Date al Signore, figli di Dio, date al Signore gloria e potenza. Salmo. Di Davide.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Date al Signore la gloria del suo nome, prostratevi al Signore in santi ornamenti.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Il Signore tuona sulle acque, il Dio della gloria scatena il tuono, il Signore, sull'immensità delle acque.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Il Signore tuona con forza, tuona il Signore con potenza.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Il tuono del Signore schianta i cedri, il Signore schianta i cedri del Libano.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Fa balzare come un vitello il Libano e il Sirion come un giovane bufalo.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Il tuono saetta fiamme di fuoco,
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
il tuono scuote la steppa, il Signore scuote il deserto di Kades.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Il tuono fa partorire le cerve e spoglia le foreste. Nel suo tempio tutti dicono: «Gloria!».
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Il Signore è assiso sulla tempesta, il Signore siede re per sempre.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Il Signore darà forza al suo popolo benedirà il suo popolo con la pace.

< Zabura 29 >