< Zabura 29 >
1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Mazmur Daud. Pujilah TUHAN, hai makhluk-makhluk surgawi, pujilah keagungan dan kuasa-Nya.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Pujilah nama TUHAN yang mulia sembahlah Dia dengan memakai pakaian ibadat.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Allah yang agung mengguntur di atas laut, suara-Nya bergema di atas samudra.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Suara TUHAN terdengar, penuh kuasa dan kemegahan.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Suara TUHAN menumbangkan pohon-pohon, mematahkan pohon cemara Libanon.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Gunung Libanon dibuat-Nya melompat seperti anak sapi, Gunung Siryon melonjak seperti anak banteng.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Suara TUHAN membuat kilat menyambar.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Suara TUHAN menggoyangkan padang gurun, TUHAN menggoyangkan padang gurun Kades.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Suara TUHAN menggoncangkan pohon-pohon berangan, dan menggugurkan daun-daun di hutan; sementara di Rumah TUHAN umat berseru, "Pujilah TUHAN!"
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
TUHAN berkuasa atas air bah, Ia berkuasa sebagai Raja untuk selama-lamanya.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Semoga TUHAN memberi kekuatan kepada umat-Nya, dan membuat mereka sejahtera.