< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Psaume de David. Rendez à l'Éternel, vous, fils de Dieu, rendez à l'Éternel la gloire et la force!
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Rendez à l'Éternel l'honneur dû à son nom; prosternez-vous devant l'Éternel dans une sainte magnificence!
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
La voix de l'Éternel retentit sur les eaux; le Dieu de gloire, l'Éternel, fait tonner sur les grandes eaux.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
La voix de l'Éternel est puissante; la voix de l'Éternel est magnifique.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
La voix de l'Éternel brise les cèdres; l'Éternel brise les cèdres du Liban.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Il les fait bondir comme un veau; le Liban et le Sirion comme un jeune buffle.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
La voix de l'Éternel jette des éclats de flammes de feu.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
La voix de l'Éternel fait trembler le désert; l'Éternel fait trembler le désert de Kadès.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
La voix de l'Éternel fait enfanter les biches; elle dépouille les forêts; et dans son temple chacun s'écrie: Gloire!
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
L'Éternel régnait au déluge; l'Éternel siégera en roi éternellement.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
L'Éternel donnera force à son peuple; l'Éternel bénira son peuple par la paix.

< Zabura 29 >